Almizan: Jarida don karuwar Musulmi

Shafin farko           

Hantsi                     

Tambaya da Amsa              

Wakilanmu             

A takaice                 

Rahotanni                

Mu leka mu gani     

Masu karatu            

Duniyarmu a yau    

Bulaliya                  

Dandalin Wasanni  

Shafin hotuna          

Shafin baya              

Taskar Almizan       

Sisters' Forum         

WasuShafuka           



Muna Facebook


 


 

Ku bimu a Twitter

  


 


Ku Tuntube mu

Muna maraba da wasikunku

 


Kash!

Ba ka sami daman kare duba tsofaffin jaridunmu ba?
Babu damuwa.
Kana iya duba nan


Ta imel a takaice,
kai tsaye

Sunanka:

Imel din ka:

Ra'ayinka:


 

Asiri ya tonu!

Makarantar Sojin Amurka na kwas din kyamar Musulunci

Wannan kwas da aka dakatar da koyar da shi a Joint Forces Staff College Virginia, daya daga cikin manyan makarantun sojin kasar, na koyar da sojin cewa babu wani sassaucin ra’ayi a addinin Musulunci, saboda haka su dauka addinin makiyinsu ne. Jami’in da ke koyar da wannan kwas din, Laftanar-Kanar Matthew Dooley, an dakatar da shi daga koyarwa, amma kuma yana rike da aikinsa a Kwalejin da ke birnin Norfolk.
    Ci Gaban Jawabin

Shin da gaske ne an haifi yaro rike da Kur’ani a hannu a Legas?

A ranar Litinin 8 ga Mayu, 2012 ne aka haifi wani jariri rike da dan karamin Kur’ani a hannunsa a wani coci mai suna White garment Church da ke Mushin, jihar Lagos a kudu maso yammacin Nijeriya.     Ci Gaban Labarin

 

Makon Sayyida Zahra (AS) a Zariya

“To, ya za a yi ka san darajar Sayyida Zahra (SA) in ba ka san bala’o’in da aka fuskanto mata da shi ba da yadda ta daure? Ita ce mai cewa an zubo min da bala’i wanda yake da yinnai aka sa ma wadannan bala’o’in da sun zama darare.” - Sayyid Zakzaky
    Ci Gaban Labarin

Gwamnatin Tarayya ce babbar ’yar Boko-haram
Janar Buhari

Tsohon Shugaban kasa, Janar Muhammadu Buhari (murabus) ya ce, gwamnatin Tarayyar Nijeriya ce babbar ’yar Boko-Haram. Ya fadi hakan ne a Kaduna, lokacin da yake jawabi ga wata tawagar wakilan jam’iyyarsa ta CPC daga jihar Neja, lokacin da suka ziyarce shi.     Ci Gaban Labarin

Kisan wani matashi a Zariya
Ya kusa kawo tarzoma

Kisan gilla da aka yi wa wani matashi da ake kira Abdullahi Nura (Fahad Baba) a Unguwar Kaura cikin birnin Zariya, ya kusa jawo wata mummunar tarzoma a garin.     Ci Gaban Labarin

Yadda wasu suka kashe dan uwa Muhammad Ali a Kano

Da sanyin safiyar ranar Juma’ar da ta gabata ne ’yan uwa na Da’irar Kano da kewaye suka shiga cikin wani yanayi na jimami da alhini na kisan wani fitaccen dan uwa, Alhaji Muhammad Ali da ke zaune a unguwar Gadon Kaya cikin birnin Kano.     Ci Gaban Labarin

Tambihi

DARASIN FIKHU 2
Tare da Muhammad Suleiman 08029493717

Kamar yadda aka ambata a darasin da ya gabata cewa, wannan darasi na Fikhu insha Allah, za a dinga gabatar da shi a bisa Usulubi na Fikhul-Mukarana ne, wato mukarana tsakanin wadannan Mazhabobi guda hudu na Ahlus-sunnah; Hannafiyya, Malikiyyah, Shafi’iyya, Hanbaliyya. A daya gefen kuma da Ja’afariyya, amma za a karfafa a Fikhun Ja’afariyya ne.
Ci Gaban Labarin

Hannun ka Mai Sanda

Sun daura damarar yaki da Musulunci

Ko mutum ya yarda ko kada ya yarda, azzaluman duniya ba su da manyan abokan gaba fiye da Musulmi da Musulunci.     Ci Gaban Labarin

Tunatarwa:
Tare da Sayyid Ibrahim Zakzaky

Sayyida Fatima Azzahra (AS)

Mai karatu yau muna dauke ne da jawabin da Sayyid Ibraheem Yaqoub Zakzaky ya yi ga dubban ’yan uwa musulmi maza da mata da suka taru a Husainiyya Bakiyyatullah Zaria ranar Juma’a 20 ga Jimada Thani, 1433, don halartar Yaumu Zahra, wanda kuma shi ne Ranar mata na duniya. Muhammad Shitu ne ya rubuta muku daga CD da muka samu daga A.M Production. Allah ya sa mu amfana.
A sha karatu lafiya.


Saurari Tafsirin Sayyid Zakzaky: 

 Farkon Suratul Muhammad (S)

 


Daga Gidan Annabta
Na Marigayi Abubakar Abdullahi Almizan

ABUBUWA 4 DA ANNABI (S) YA UMURCI SAYYIDA FATIMA (AS)

An ruwaito daga Sayyida Zahra (AS) ta ce; “Manzon Allah (S) ya shiga gare ni a lokacin na yi shimfida don in yi barci, sai ya ce da ni ya Fatima kar ki yi barci har sai kin yi abubuwa hudu; sauke Alkur’ani, sanya Annabawa masu cetonki, ki yardar da Muminai a kanki, ki yi Hajji da Umra. Ki aikata wadannan.

Sai ya ci gaba da yin Salla, ta yi hakuri har ya idar. Sai ta ce; “Ya Rasulillah (S)! Ka umurce ni da abu hudu da ba zan iya yin su a wannan halin ba”. Sai ya yi murmushi, ya ce; “Idan kika karanta Kulhuwallahu kafa uku tamkar kin sauke Alkur’ani ne. Idan kika yi salati a gare ni da sauran Annabawa za su sanya cetonki a ranar alkiyama. Idan kika roki gafara ga Muminai za su yarda da ke gaba dayansu. Idan kika ce, ‘Subhanallah, Walhamdulillah, Wala’ilahaillalah, Wallahu Akbar’, kin yi Hajji da Umra.

Don karin bayani a duba Mufatihul Jinan babi na 6, shafi na 766.

Daga Alkazeem M. Al-Hassan, 08062740226.


Hotunan wannan mako: