Jama’a sun fasata da NLC
Jama'a sun fusata matuka da matakin da kungiyar kwadago, NLC, ta kasa ta dauka na mika wuya ga tayin Naira 97 ga litar mai da gwamnatin Goodluck Jonathan ta bayar, inda ta bukaci kowa ya koma bakin aikinsa duk da kuwa a baya suna korarin cewa ba za su koma bakin aiki ba, matsawar an kara kudi a kan Naira 65.
Jama'a da dama a Kano, Kaduna da Legas sun bijire wa umurnin uwar kungiyar kwadago ta kasa da ta bukaci mutane su ci gaba da zama don yajin aiki a ranar Litinin, amma kar su fito zanga-zangar adawa da cire tallafin mai da gwamnatin Goodluck Jonathan ta yi.
Ci Gaban Jawabin
Tweet
Mutumin da ake zargi da kai hari a wani Coci da ke Garin Madalla, Suleja ranar Kirsimeti, kuma aka ba da sanarwar cafke shi ranar Asanar da ta gabata, mai suna Kabiru Sakkwato, a halin yanzu dai ya tsere daga hannun ’ya sandan dake tsare da shi. Wanda kuma wannan ya sa hukumar ’yan sandan ta kasa ta dakatar da Kwamishian ’yan sanda, Zakari Biu, wanda shi ke da alhakin kula da gudnar da binciken.
Ci Gaban Labarin
Tweet
Jama’a sun koka matuka da matakin cin zarafin Alkur’ani mai tsarki da wasu daga cikin sojojin rundunar musamman don wanzar da zaman lafiya (JTF) ke yi a yankin Ummarari da ke Maiduguri babban birnin Jihar Borno.
Ci Gaban Labarin
Tweet
Ranar Litinin da ta gabata ne jami’an soja a Kaduna suka gabatar da tsohon Shugaban kungiyar direbobin tanka ta Kaduna, kuma Marafan Narasawa Kaduna, Kwamared Nuhu Muhamamd da dansa Musa ga manema labarai bisa zarginsa da mallakar bindigogi da sauran wasu makamai ba bisa ka’ida ba, wanda kuma Lauyansa ya ce wannan kamu yana cike da siyasa. Ci Gaban Labarin
Tweet
’Yan uwa Musulmi almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky na wannan kasa sun bi sahun ’yan uwansu na duniya ta hanyar yin tattaki a kafa zuwa taron juyayin kwana 40 da shahadar Imam Husaini (AS), inda suka taka daga sassa daban-daban na kasar nan zuwa Husaniyyar Bakiyyallah, Zariya.
Ci Gaban Labarin
Tweet
Wata jaridar London da ake kira SUNDAY TIMES ta bayyana cewa jami’an Hukumar leken asiri na Haramtacciyar Isra’ila, MOSSAD ce ke da alhakin kisan dauki dai-dai da aka yi wa wani masanin fasahar nukiliyar Iran a makon jiya.
Ci Gaban Labarin
Tweet
Tambihi
Arba’in din Imam Husain (AS)Tare da Muhammad Suleiman 08029493717
Ranar Arba’in din Imam Husain (AS) rana ce wadda take da muhimmanci, musamman ga mabiya Ahlul Baiti (AS). Kuma kiyaye ranar yana daga cikin alamomin Mumini, kamar yadda haka ya zo daga Imam Hasan Al’askari (AS), inda ya ce; “Alamomin Mumini (wato dan Shi’a) guda biyar ne. 1. Yin Salla raka’a 51 ko wace rana, 2. Ziyarar Arba’in. 3. Sa zobe a dama. 4. Sa goshi a kasa (ta’afir). 5. Bayyana karatun Bismillah a Salla”.
Ci Gaban Labarin
Tweet
Hannunka mai Sanda
Zanga-zangar cire tallafin mai
Tabbatar da karin kudaden albarkatun man fetur da cire tallafin gwamnati, wani rashin imani ne gami da kokarin aiwatar da muradun Amurka da sauran kasashen Turai.
Ci Gaban Labarin
Tweet
